Firministan kasar Sin Li Keqiang ya yi kira ga mahukuntan lardunan tsakiya da na yammacin kasar Sin, da su zage damtse waje bunkasa tattalin arzikin yankunansu.
Mr. Li ya bayyana hakan ne yayin ziyarar aiki ta kwanaki uku da ya gudanar a wadannan yankuna, inda ya zanta da al'ummun kauyuka, da yankunan dake wadannan shiyyoyi, ciki hadda al'ummun kananan kabilu, da na biranen lardin Guizhou dake kudu maso yammacin kasar ta Sin.