An dai gudanar da wannan biki ne a ranar Laraba 3 ga watan nan, inda aka kaddamar da shirin tura wadannan jami'ai kasashen Laberiya, da Saliyo da kuma Guinea, domin su taimaka wajen yaki da cutar Ebola. Rahotanni sun bayyana cewa gwamnatin Najeriyar da hadin kan kungiyar tarayyar Afirka AU ne suka dauki nauyin tura ma'aikatan kiwon lafiyar 250 zuwa wadannan kasashe.