in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Kasar Sin tayi alkwarin karfafa zumuncin ta da kasar Brazil
2014-10-27 20:34:45 cri
Kasar Sin ta yi alkawarin karfafa zumunci da kasar Brazil ta kowane bangare, inji kakakin ma'aikatar harkokin wajen Sin Madam Hua Chunying a ranar Litinin din nan lokacin ganawar ta da manema labarai.

Da take amsa tambayoyin daga manema labaran game da sake zaben shugaban kasar mai ci yanzu Madam Dilma Rouseff, Madam Hua ta ce Shugaban kasar Sin Xi Jinping tuni ya riga ya aike da sakon taya murna ga Shugaba Rouseff bisa ga wannan nasara.

Madam Hua ta yi bayanin cewa Kasar Sin ta dade tana dora muhimmanci tare da duba zumuncin dake tsakaninta da Brazil tun da ba yau ba a don haka a shirye take ta kara karfafa wannan zumuncin bisa ga amincewa da juna, kara sabbin hanyoyin yin hulda da juna da kuma daukaka wannan zumunci zuwa wani sabon mataki.(Fatimah Jibril)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China