in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Ministan harkokin wajen kasar Sin ya bayyana nasarar da shugaban kasar Sin ya cimma a ziyarar da ya kai a kasashen yankin tsakiya da kudancin Asiya
2014-09-20 11:54:54 cri
Daga ranar 11 zuwa 19 ga wata ne, shugaban kasar Sin Xi Jinping ya halarci taro karo na 14 na hukumar kungiyar hadin gwiwa ta Shanghai(SCO) kana ya kai ziyarar aiki a kasashen Tajikistan da Maldives da Sri Lanka da kuma Indiya. A dab da kammalar ziyarar, ministan harkokin wajen kasar Sin ya bayyana wa manema labarai ma'anar wannan ziyarar, inda a cewarsa, ziyarar ta bude wani sabon babi na sada zumunta da hadin gwiwa tsakanin kasar Sin da makwabtanta, kana ta bude kafar bunkasa yankin tattalin arziki da hanyar siliki ta ratsa da kuma hanyar siliki ta kan teku cikin karni na 21.

Ministan ya ce, yankunan tsakiya da kudancin Asiya muhimman sassa ne na nahiyar Asiya da Turai. Kasashen hudu da shugaban kasar Sin ya ziyarta a wannan karo dukkansu muhimman kasashe ne da hanyar siliki ta ratsa a zamanin da, wadanda kuma suka fara cudanya tare da kasar Sin tun lokacin da. Kasashen sun kasance muhimman madogarai wajen bunkasa yankin tattalin arziki da hanyar siliki ta ratsa da kuma hanyar siliki ta kan teku cikin karni na 21. Shugaban kasar Sin ya kai wannan ziyara ce bisa yin la'akari da halin da ake ciki a gida da kuma waje. Manufar bunkasa yankin tattalin arziki da hanyar siliki ta ratsa da kuma hanyar siliki ta kan teku cikin karni na 21 ita ce hada kan al'ummar kasashen da zummar tabbatar da zaman lafiya da kwanciyar hankali da kuma ci gaban sassan.(Lubabatu)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China