in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Shugabannin Afrika 6 za su halarci taron AU kan ta'addanci a Kenya
2014-09-02 09:43:47 cri

Shugabannin kasashen Afrika shida ne za su halarci wani zaman taro na kwamitin zaman lafiya da tsaro (CPS) na kungiyar tarayyar Afrika (AU) da zai gudana a birnin Nairobi na kasar Kenya domin tattauna kan barazanar tsaro a nahiyar, in ji ministan harkokin wajen kasar Kenya a ranar Litinin.

Ministan ya bayyana a cikin wata sanarwa cewa, shugabannin Chadi, Nijar, Najeriya, Somaliya, Tanzaniya da Uganda sun tabbatar da zuwan nasu a wannan babban dandali na yini guda da za'a fara a ranar Talata a Nairobi.

Makasudin wannan taro shi ne kaddamar da wani cikakken nazari kan wannan matsala da kokarin da kungiyar AU take yi a halin yanzu domin yaki da ta'addanci a nahiyar Afrika bisa tsarin dokoki da matakan aikin da suka dace na kungiyar tarayyar Afrika AU, in ji wannan sanarwa. (Maman Ada)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China