in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Firaministan Lesotho ya tsallaka Afirka ta Kudu sakamakon juyin mulki
2014-08-31 16:49:37 cri
Rundunar soji a Lesotho ta mamaye hedkwatar rundunar 'yan sanda dake babban birnin kasar Maseru a jiya Asabar, bayan da ta yiwa fadar firaministan kasar kawanya. A wani mataki na juyin mulki don neman kawo karshen gwamnati mai ci kamar yadda firaministan kasar Thomas Thabane ya yi zargi.

Rahotanni sun ce tuni Mr. Thabane ya tsallaka kasar Afirka ta Kudu, yayin da kuma a Lahadin nan rundunar sojin kasar da 'yan sanda suka yi musayar wuta ta tsahon sa'o'i uku, koda yake dai an ce ba a samu asarar rayuka ya yin musayar wutar ba.

Kaza lika rundunar sojin ta hana amfani da hanyoyin sadarwar gidajen radiyo, da na talebijin da dai sauransu.

Tuni dai firaministan kasar ta Lesotho ya tabbatarwa wani gidan talabijin dake kasar Afirka ta Kudu aukuwar juyin mulkin kasar ta sa. Ya kuma bayyana wa wani gida rediyon kasar Burtaniya cewa, zai tattauna da wasu shugabannin kasar Afirka ta Kudu, da ke wakiltar kungiyar bunkasa kudancin Afirka ta SADC kan yanayin da Lesothon ke ciki. Kana ya na fatan komawa gida da zarar an samu yanayi na tsaron lafiyar sa. (Maryam)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China