in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Sojojin Lesotho sun yi ma hedkwatar 'yan sanda kawanya
2014-08-30 20:38:57 cri
Rundunar sojojin kasar Lesotho ta yi wa hedkwatar 'yan sanda kawanya a Maseru, bisa wata jita-jitar juyin mulki, a yayin da gwamnatin kasar ta bayyana cewa har yanzu ta bisa kan mulki.

Rundunar sojojin kasar sun killace hedkwatar 'yan sanda, in ji Thesele Maseribane, ministan wasannin motsa jiki kana shugaban jam'iyyar Basotho National Party a wata hirarsa da 'yan jarida.

Kamfanin dillancin labarai na South African Broadcasting Corporation (SABC) ya ambato wani ofisa a cikin hedkwatar 'yan sanda na cewa an killace su.

Mista Maseribane ya ambato wani yunkurin juyin mulki a cikin wannan karamar masarauta da kasar Afrika ta kudu ta kewaye. Haka kuma sojojin sun dakile hanyoyin sadarwa na rediyo. Amma duk da haka, ministan ya jaddada cewa gwamnatin kasar tana bisa ikonta.

Faraministan kasar Thomas Thabane da ni kaina muna cikin gwamnatin hadaka. Faraminsta yana kan ikonsa kuma yana cikin koshin lafiya, in ji mista Maseribane.

Kaftan Ntlele Ntoi, kakakin rundanar sojojin Lesotho ya bayyana cewa sojojin sun dauki wannan matakin bayan sun samu bayanan dake nuna cewa wasu ofisoshin 'yan sanda suna shirin mikawa wani gungun 'yan siyasa na kusa da faraminista makamai da harsasai. (Maman Ada)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China