A nasa bangare, babban jami'in dake kula da harkokin al'adu na ofishin jakadancin Sin dake Najeriya Mista Yan Xiangdong ya ce, nuna fasahohin yin zane-zanen gargajiya gami da dafa shayi na kasar Sin, ya zama wani muhimmin bangare ta fannin yada al'adun kasar Sin ga al'ummar Najeriya. Ya ce a nan gaba ma, cibiyar al'adun kasar Sin dake Najeriyar zata ci gaba da kokarinta na gayyatar kwararru a fannonin zane-zanen gargajiya da dafa shayi, don karawa 'yan Najeriya fahimta game da kyawawan fasahohin gargajiyar Sin. (Murtala)