in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Ministocin harkokin wajen kasashen dake makwabtaka da Libya sun yi ganawa a Algeria
2014-05-30 14:24:42 cri
Jiya Alhamis 29 ga wata, ministan harkokin wajen kasashen kewayen kasar Libya sun yi ganawa a birnin Algiers na kasar Algeria inda suka yi kira ga bangarorin da rikicin kasar Libya ya shafa da su yi shawarwari wajen warware sabanin dake tsakaninsu, ta yadda za a iya shimfida zaman lafiya mai karko a kasar.

Ministocin harkokin wajen kasashen Algeria, Masar, Sudan da kuma Tunisia sun yi shawarwari kan yanayin kasar Libya a yayin da suka halarci taron ministoci karo na 17 na kungiyar kasashe 'yan ba ruwanmu. A yayin ganawar tasu, ministocin kasashen hudu sun cimma matsaya guda wajen sa kaimi ga bangarorin da abin ya shafa na kasar Libya da su yi shawarwarin a duk fadin kasar, da kuma kiyaye yanayin zaman karkon kasar tun bayan kifar da gwamnatin Mohamar Kaddafi, bugu da kari, sun kuma yi kira ga bangarorin da abin ya shafa da su girmama hukumomin kasar, ciyar da yunkurin dimokuradiyya gaba cikin yanayin zaman lafiya da na zaman karko. (Maryam)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China