in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Bankin duniya zai tallafawa Afrika kaddamar da ayyukan inganta jin dadin rayuwar jama'a
2014-05-30 11:03:25 cri

Bankin duniya ya ce, ya ware bashin dalar Amurka biliyan 10, domin tallafawa ayyuka dabam-dabam na inganta jin dadin rayuwa jama'ar kasashen Afrika tare da bunkasa tattalin arzikinsu.

Mataimakin shugaban bankin duniya Makhtar Diop shi ne ya bayyana hakan a Maputo, a lokacin wani taron kwanaki biyu na farfado da Afrika, wanda gwamnatin Mozambique da asusun bayar da lamuni na duniya IMF suka shirya.

A yayin da take jawabi a kan taron, Diop ya ce, akwai matakai dabam dabam da suka wajaba da za'a dauka domin kawo sauyi a Afrika a kokarin da ake yi na bunkasa habbakar tattalin arziki a nahiyar.

Darektan asusun IMF Christine Lagarde ta gana a ranar Alhamis da ministocin harkokin kudi da kuma shugabannin bankunan kasashen Afrika, wadanda dukanin su sun halarci taron.

Lagarde ta ce, hasashe na nuni da cewar, za'a sami haske a kokarin da ake yi na bunksa tattalin arzikin nahiyar ta Afrika. (Suwaiba)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China