in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Najeriya ta karyata jita jitar annobar cutar Ebola a cikin kasar
2014-04-02 10:14:39 cri

Babu wasu yankunan da aka gano annobar cutar Ebola a tarayyar Najeriya, in ji gwamnatin wannan kasa dake yammacin nahiyar Afrika, domin kawo karshen jita jitar dake bayyana cewa, an samu bullowar wannan cuta mai haddasa zubar da jini dake kuma kashewa nan take. Amma ana sanya ido a halin yanzu a cikin wasu yankunan wannan kasa, mafi yawan mutane a Afrika, wani nau'in cutar Dengue ita ma da ke haddasa zubar da jini da ake dauka ta hanyar cizon sauro dake dauke da kwayoyinta, in ji sakataren kasa kan harkokin kiwon lafiya mista Khaliru Alhassan a yayin da yake hira tare da 'yan jarida a birnin Abuja. Labaran da ake watsa wa kan bazuwar cutar Ebola a cikin wannan kasa ba su da tushe ko kadan, in ji jami'in. (Maman Ada)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China