in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
'Yan Cote D'Ivoire sama da 100 sun janye jiki daga jamhuriyar Afrika ta tsakiya
2013-12-31 12:58:43 cri
A ranar 30 ga wata, 'yan kasar Cote D'Ivoire da yawansu ya kai 123 da suka janye daga jamhuriyar Afrika ta tsakiya sun isa birnin Abidjan na kasarsu.

Sakamakon tabarbarewar yanayin tsaro da jamhuriyar Afrika ta tsakiya ke fuskanta, kasar Cote D'Ivoire ta yanke shawarar tura jirgin saman musamman domin kwashe jama'arta daga jamhuriyar Afrika ta tsakiya.

Ana ta yi tashin hankali a jamhuriyar Afrika ta tsakiya. A watan Maris na bana ne, 'yan tawayen Seleka suka hambarar da mulkin shugaban kasar François Bozizé. A cikin Afrilu, an kafa gwamnatin wucin gadi ta kasar, inda aka zabi Michel Djotodia jagoran 'yan Seleka a matsayin shugaban kasa na wucin gadi na kasar. Kwanan baya, an kara tsananta rikicin dake tsakanin dakarun 'yan Seleka da dakaru masu tsaron kansu na kasar, lamarin da ya haddasa hargitsin jin kai mai tsanani.

A ranar 26 ga wata, babban magatakardan M.D.D. Ban Ki-moon ya ba da wata sanarwa, inda ya nuna mamaki sosai kan rikicin da aka ta samu a Afrika ta Tsakiya, a sa'i daya kuma, ya bukaci bangarori daban daban da su samar da dama mai kyau don kare fararen hula, tare da kiyaye zaman lafiya da farfado da oda a kasar.(Bako)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China