in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Kasar Sin za ta goyi bayan kasar Kenya game da shari'ar da ake yiwa shugabannin kasar
2013-11-19 19:00:50 cri
Kakakin ma'aikatar harkokin wajen kasar Sin Hong Lei, ya bayyana kudurin kasar Sin na ci gaba da goyon bayan kasar Kenya da kungiyar tarayyar Afirka (AU) bayan da kwamitin sulhu na MDD ya ki goyon bayan a jinkirta shari'ar da ake yiwa shugaban kasar Uhuru Kenyatta da mataimakinsa William Ruto a kotun ICC.

Mr Hong Lei ya bayyana hakan ne a ranar Talata yayin taron manema labarai, inda ya bayyana rashin jin dadinsa matuka game da gazawar kwamitin sulhun na gabatar da wani kuduri game da jinkirta shari'ar da kotun ICC ke yiwa shugabannin biyu.

Hong ya ce, kasar Sin ta yi imanin dewa, batutuwan da suka shafi zaman lafiya da kwanciyar hankalin nahiyar Afirka, kamata ya yi kwamitin sulhu ya saurare su da idon basira kana ya gabatar da wani kuduri da zai dace da muradun AU da sauran kasashen Afirka.

Kasar Sin tana goyon bayan matakin da kasashen Afirka suka dauka kana ta kada kuri'ar amincewa da wannan kuduri, yana mai cewa, kasar Sin za ta ci gaba da goyon bayan kokarin da suke yi na samo bakin zaren warware wannan matsala. (Ibrahim)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China