Ministan tsaron kasar Sudan Abdul-Rahim Mohamed Hussein ya ayyana fara wani gagarumin kamfel din kai harin soja, da nufin kawo karshen ayyukan masu tayar da kayar baya a yankin Darfur da jihohin Blue Nile da kudancin Kordofan da ke iyaka da kasar Sudan ta Kudu.
Ministan ya bayyana hakan ne ranar Talata cikin wata sanarwa da ya gabatarwa majalisar dokokin kasar, inda ya ce, kasarsa ta kimtsa kuma ta tura dakaru zuwa sassa daban-daban na wadannan yankunan da nufin dakile ayyukan masu tayar da kayar baya.
Bugu da kari, ya zargi 'yan tawayen Revolutionaey Front, wadanda ke kwance da kungiyoyi hudu masu dauke da makamai da zummar halaka jama'a da sace mutane a wasu manyan birane.
Tun da farko dai shugaba Omar al-Bashir na kasar Sudan, ya lashi takwabin kawo karshen dukkan tashin hankali da fadace-fadacen da ake samu tsakanin kungiyoyi masu dauke da makamai a dukkan sassan kasar ya zuwa karshen shekarar 2014. (Ibrahim)