in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Bankin raya Afirka ya yi hasashen ci gaban tattalin arzikin nahiyar
2013-08-08 14:23:22 cri

A yayin da kasashen dake nahiyar Turai ke kokawar fidda kai daga tarin matsalolin tattalin arziki dake addabarsu, a hannu guda bankin bunkasa kasashen Afirka ADB, ya yi hasashen ci gaba da bunkasar nahiyar Afirka ta fuskar tattalin arziki cikin 'yan shekaru masu zuwa.

Wani rahoto da bankin ya fitar a birnin Johannesburg na kasar Afirka ta Kudu a ranar Laraba, ya nuna cewa, a bana, nahiyar za ta samu karin ci gaban tattalin arziki da kaso 4.8 cikin dari, yayin da a shekarar 2014, mizanin ci gaban zai karu zuwa kaso 5.3 cikin dari

A cewar babban jami'i a sashen nazarin tattalin arzikin bankin na ADB Mthuli Ncube, kasashen yammacin Afirka da suka hada da Saliyo, da Ivory Coast da Ghana, su ne za su zama a kan gaba, wajen karuwar tattalin arziki bisa ma'aunin GDP, a tsakanin shekarun 2013 zuwa 2014.

Wannan matsayi, a cewar Ncube, zai sanya yankin yammacin Afirka, zama mafi samun ci gaba a wannan fanni, idan aka kwatanta da ragowar sassan nahiyar. (Saminu)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China