in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Shugaban kasar Sudan ya karbi bakuncin wakilin kasar Sin na musamman mai kula da harkokin Afirka
2013-07-26 10:37:03 cri
A ranar Alhamis ne shugaban kasar Sudan Omar al-Bashir, ya karbi bakuncin wakilin gwamnatin kasar Sin na musamman mai kula da harkokin Afirka Zhong Jianhua.

A cewar wata sanarwa da ofishin jakadancin kasar Sin da ke Khartoum ya bayar, wadda kamfanin dillancin labarai na Xinhua ya samu kwafinta, ana saran yayin tattaunawar da za su yi bangarorin biyu za su yi musayar ra'ayoyi game da dangantakar da ke tsakaninsu, da kuma yanayin da ake ciki tsakanin Sudan da Sudan ta kudu.

Bugu da kari sanarwar ta ce, Zhong ya tattaunawa da ministan harkokin wajen kasar Sudan Ali Karti, ganawar da ta samu halartar jakadan Sin da ke Khartoum Luo Xiaoguang, darekta mai kula da harkokin kasar Sin a ma'aikatar harkokin wajen kasar Sudan.(Ibrahim)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China