in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Ministoci biyu na kasar Gabon sun lashi takobin murkushe 'yan fashin teku
2013-07-22 11:14:30 cri
Ministan tsaron kasar Gabon, Pacome Rufin Ondzounga da takwaransa na cikin gida, Jean Francois Ndongou, sun kai wani rangadin aiki a birnin Port-Gentil yankin hakar man fetur kuma cibiyar tattalin arzikin kasar Gabon, domin sanar da maida martanin da aka shirya kan murkushe 'yan fashin teku da suka dauki yin daga da kasar bayan da suka yi garkuwa da wani jirgin ruwan jigilar man fetur da ya zo daukar dayen man fetur a tashar ruwan Cap Lopez, a wani labarin da aka samu a ranar Lahadi daga ma'aikatar tsaron kasar Gabon.

A ranar 15 ga watan Julin da ya gabata ne, 'yan fashin teku da ake zaton 'yan asalin kasar Najeriya sun yi garkuwa da jirgin ruwan Tanker Cotton mai lambar IMO 9380380 tare da mambobin jirgin ruwan 24 'yan asalin kasar Indiya a yayin da jirgin zuwansu ya zo daukar gurbataccen man fetur a tashar ruwan Cap Lopez. (Maman Ada)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China