in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Gwamnan Kano a tarayyar Nijeriya ya jagoranci kona jabun magunguna na sama da naira miliyan 900
2013-06-17 16:28:15 cri

 

Gwmanan Kano a tarayyar Najeriya Injiniya Rabi`u Musa Kwankwaso ya jagoranci bikin kone wasu jabun magunguna masu tarin yawa da aka kama a unguwar Farawa dake yankin birnin Kano.

Daga cikin magungunan da aka kona sun hada da na Tari, da na kashe kwayoyin cuta da magungunan ciwon ido da ciwon kunne da mayikan shafawa a kuraje da allurai da kuma wasu lemukan sha wadanda wa`adin aikin su ya kare.

Wannan dai ba shi ne karo na farko ba da gwamnan jihar Kano Injniya Rabi `u Musa Kwankwaso ya jagoranci kone jabun magunguna da sauran kayan abinci da wa`adin amfani da su ya kare, tun bayan kasancewarsa gwamna a tsawon shekaru biyu da suka gabata.

Rahotanni sun bayyana cewa ya zuwa yanzu gwamnatin Kano ta lalata irin wadannan kayayyaki da kudinsu ya kai sama da naira buliyan biyu.

Da yake jawabi bayan an cinnawa magungunan wuta, Gwamna Rabi`u Musa Kwankwaso ya ce abun takaici duk da kokarin da gwamnatinsa ke yi na dakile cinikin jabun magunguna a jihar, amma sai ga shi wasu batagari suna bin haramtattun hanyoyin shigo da irin wadannan magunguna ba tare da tunanin illolin dake tattare da yin hakan ba ga yanayin lafiyar al`umma.

1 2
Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China