in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Wata tawagar kungiyar SADC ta isa tsibirin Madagascar
2013-05-03 10:27:29 cri

Wata hadadiyyar tawagar kungiyar cigaban kasashen kuriyar Afrika ta kungiyar SADC dake karkashin jagorancin tsohon shugaban kasar Mozambique Joachim Chissano ta isa tun ranar Alhamis da yamma a Antananarivo, babban birnin tsibirin Madagascar, domin sa ido kan cigaban da aka samu wajen shirye-shiryen zabubuka a wannan kasa, a cewar wata sanarwar ma'aikatar harkokin wajen kasar da aka fitar a ranar Alhamis. Tun zuwan wannan tawaga, mista Joachim Chissano ya bayyana wa 'yan jarida cewa, wannan ziyara tasa na nauyin kimanta cigaban da aka samu game da shirye-shiryen zabubuka a wannan babban tsibiri, tare jaddada muhimmancin gudanar da zabubuka kamar yadda hukumar zabe ta kasa mai zaman kanta ta rikon kwarya CENIT ta tsara.. (Maman Ada) 

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China