in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Ziyarar da Jia Qinglin ya yi a Afirka ta samu sakamako sosai
2010-04-02 21:29:23 cri

Bisa gayyatar majalisar dokokin Kamaru, kwamitin harkokin kasa na Namibiya, da kuma kwamitin harkokin larduna na Afirka ta Kudu, Jia Qinglin, shugaban majalisar ba da shawara kan harkokin siyasa ta kasar Sin wato CPPCC ya yi ziyarar sada zumunci a kasashen 3 daga ran 23 ga watan jiya zuwa ran 1 ga wata.

A kan hanyarsa ta dawowa kasar Sin, Wang Shenghong, mataimakin sakataren majalsar CPPCC ya yi wa manema labaru bayani kan ziyarar. A ganinsa, ziyarar da Mr. Jia Qinglin ya yi a Afirka na matsayin muhimmin matakin diplomasiyya ne da kasar Sin ta dauka domin aiwatar da sakamakon da aka samu a yayin taron ministoci a karo na 4 na dandalin tattaunawar yin hadin gwiwa a tsakanin Sin da kasashen Afirka daga dukkan fannoni da sa kaimi kan raya huldar abokantaka ta sabon salo a tsakanin Sin da kasashen Afirka bisa manyan tsare-tsare. Haka kuma, ziyarar na da muhimmiyar ma'ana a fannonin zurfafa dadadden zumuncin dake tsakanin Sin da kasashen 3 da inganta hadin gwiwa da hada kai a tsakanin Sin da kasashen Afirka.

Mr. Wang ya kara da cewa, a lokacin ziyararsa, Mr. Jia Qinglin da shugabannin kasashen 3 sun sami ra'ayi daya kan raya hulda a tsakanin Sin da kasashensu da kyautata hadin gwiwa a tsakanin Sin da Afirka, hakan ya inganta hulda a tsakanin Sin da kasashen 3 da kuma kafa harsashin siyasa a tsakanin Sin da Afirka wajen bunkasa zumuncinsu.

1 2
Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China