Facebook Twitter
in Web hausa.cri.cn
Wakilin Sin ya yi kira da a kawar da talauci don ingiza tabbatar da hakkin dan Adam
2020-09-23 11:14:32        cri
Zaunannen wakilin Sin dake ofishin MDD a Geneva da ofishin kungiyoyin kasa da kasa a kasar Switzerland Chen Xu ya yi jawabi a madadin kasashen Asiya da Afirka da Latin Amurka kimanin 80 kan batun kawar da talauci don sa kaimi ga tabbatar da kare hakkin dan Adam a gun taro na 45 na majalisar kare hakkin dan Adam ta MDD a jiya.

Chen Xu ya bayyana cewa, kimanin mutane miliyan 800 ne suke fama da talauci a duniya, musamman bayan barkewar cutar COVID-19, kuma akwai yiwuwar mutane miliyan 71 za su sake fadawa kangin talauci. Hakan zai tsananta matsalar rashin daidaito a cikin al'umma, da kawo illa kan yadda ake kiyaye hakkin dan Adam a duniya baki daya.

A don haka, Chen Xu ya yi kira ga kasashen duniya, da su ba da muhimmanci ga aikin yaki da talauci don bunkasa tattalin arziki, da taimakawa yaki da talauci ta sabbin hanyoyi a lokacin da bukatar hakan ta taso, da sa kaimi ga yaki da talauci, da bunkasa tattalin ariki da zamantakewar al'umma da al'adu, da kiyaye muhalli, da kuma kiyaye hakkin dan Adam baki daya. Kana ya yi kira ga kasashen duniya, da su maida hankali kan bukatun jama'a, ta hanyar inganta rayuwarsu, da bullo da tsarin bada inshora ga zamantakewar al'umma, da rage tasirin da masu fama da talauci suka fuskanta a sakamakon cutar COVID-19, da kara gina ayyukan more rayuwa a yankuna masu fama da talauci, da samar da hidimar kiwon lafiya, da bada ilmi, da al'adu, da likitanci ga masu fama da talauci, da kuma kara samar musu da ayyukan yi, don kara karfinsu na dogaro da kai. (Zainab)

 

Labarai masu Nasaba

 

 

 

 

Mafiya Karbuwa

 

 

 

 

® China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China