in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
An gudanar da bikin mika aikin gina makarantun firamare na gwamnatin Sin ga Burkina Faso
2019-04-21 17:23:31 cri
An gudanar da bikin mika aikin gina makarantun firamare na gwamnatin Sin ga Burkina Faso a birnin Ouagadougou na kasar a ranar Juma'a, wanda ya samu halartar ministan kula da bada ilmi da yaki da jahilai da yada yaren kabilun kasar Stanislas Ouaro da jakadan Sin dake Burkina Faso Li Jian da sauran wasu jami'ai.

Minista Ouaro ya bayyana cewa, Sin da Burkina Faso sun sake kulla dangantakar diplomasiyya a tsakaninsu cikin kasa dashekara daya, inda aka samu nasarori da dama karkashin hadin gwiwarsu. Ya ce a fannin bada ilmi, Sin ta gina makarantun firamare guda biyu ga kasar Burkina Faso a cikin gajeren lokaci, kana za ta kara gina makarantun firamare 100 a kasar, wannan ya shaida sahihanci da karfinsu a wannan fanni. Ya ce ya yi imani cewa, kasashen biyu za su ci gaba da yin kokari tare wajen zurfafa hadin gwiwar dake tsakaninsu.

A nasa bangare, jakada Li Jian ya bayyana cewa, gwamnatin kasar Sin za ta ci gaba da yin kokarin kyautata yanayin bada ilmi na kasar da kuma sa kaimi ga raya hadin gwiwarsu a wannan fanni. (Zainab)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China