Mataimakin jami'in mai bada umurni na 'yan sanda na kasar Somaliya Hossain ya bayyana cewa, bom da aka ajiye a cikin wata mota ya fashe a kofar wani dakin cin abinci dake birnin Mogadishu a wannan rana. Ya zuwa yanzu, an tabbatar da cewa, mutane 4 sun mutu kuma mutane 5 sun ji rauni a sakamakon harin, watakila yawan mutanen da suka mutu zai karu.
Har zuwa yanzu, babu wata kungiya da ta sanar da daukar alhakin harin ba. amma manazarta sun yi hasashen cewa, kungiyar Al-shabaab ce ke kai hare-hare irin kamar hakan. (Zainab)