in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Hukumomin MDD sun hada hannu wajen taimakawa wadanda mahaukaciyar guguwar Idai ta shafa
2019-04-17 10:50:53 cri
Hukumar samar da abinci da kula da aikin gona da hukumomin kula da yara na MDD, sun hada hannu wajen taimakawa mutanen da mahaukaciyar guguwar Idai ta shafa a kasashen Mozambique da Zimbabwe da Malawi na yankin kudancin Afrika a cikin watan da ya gabata.

Yayin taron manema labarai, Stephane Dujarric, kakakin Sakatare Janar na MDD, ya ce tun bayan da mahaukaciyar guguwar Idai ta aukawa kasar Mozambique cikin tsakiyar watan Maris, hukumar samar da abinci ta MDD WFP, ta tallafawa mutane miliyan 1 da abinci a kasar.

A Zimbabwe kuwa, asusun bada agajin gaggawa ga yara na MDD, ya sanar da cewa, an fara bayar da rigakafin cutar kwalara na sha, ga mutane 488,000 a jiya Talata, a larduna biyu da guguwar ta fi shafa.

Sama da mutane 1,000 ne mahaukaciyar guguwar Idai da ruwan sama da ambaliya suka yi sanadin mutuwarsu. Har kawo yanzu, Dubban mutane ne ke bukatar agaji bayan aukuwar iftila'in.

Bankin duniya ya yi kiyasin cewa, kasashen da iftila'in ya shafa na bukatar dala biliyan 2 domin su farfado. (Fa'iza Mustapha)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China