in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
'Yan adawar kasar Sudan sun bukaci a sanya fararen hula cikin gwamnatin kasar
2019-04-14 16:14:36 cri
Kungiyar kawance mai fafutukar 'yanci da sauyi ta Sudan wato Freedom and Change Alliance, ta bukaci kwamitin mulkin soji na wucin gadi na kasar, ya sanya fararen hula cikin harkokin tafiyar da gwamnati.

Kungiyar ta yi kiran ne lokacin da ta gana da Abdel-Fattah Al-Burhan, shugaban kwamitin mulkin soji na kasar.

Daya daga cikin mambobin kungiyar Omer Al-Digair, ya bayyanawa manema labarai cewa, baya ga gwamnatin farar hula, suna bukatar a shigar da fararen hula cikin majalisar shugabancin kasar na wucin gadi.

Ya ce kungiyar za ta gabatar da jerin bukatunta ga shugaban na rikon kwarya a yau Lahadi.

Omer Al-Digair, ya kuma ce kungiyarsu ta bukaci kwamitin sojin ya sake fasalin hukumar tsaron kasar tare da hukunta dukkan wadanda ke da hannu a laifukan cin hanci da kashe masu zanga-zanga. (Fa'iza Mustapha)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China