in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
An fitar da rukunin kasashen da za su fafata a gasar cin kofin Afrika na bana
2019-04-13 17:09:59 cri
An fitar da rukunin kasashen da za su fafata a gasar cin kofin Afrika na bana, wato AFCON 2019 a takaice, a wani kayataccen biki da aka yi a Dalar Giza ta Masar, mai cike da tarihi.

A rukuni na A, Masar mai masaukin baki, za ta fafata da kungiyar Leopards ta Jamhuriyar Demokradiyyar Congo da kungiyar Cranes ta Uganda da kuma Warriors ta kasar Zimbabwe.

Masar da Zimbabwe ne za su bude gasar ta AFCON na bana, wadda za a fara ranar 21 ga watan Yuni.

A rukunin B kuma, kungiyar Super Eagles ta Nijeriya za ta fafata da takwararta ta National Sily ta kasar Guinea da kuma Burundi da Madagascar, wadanda suka samu cancantar shiga gasar AFCON a karon farko.

Senagal kuma za ta barje gumi a Rukuni na C da kasashen Tanzania da Kenya da kungiyar Fennecs ta Aljeria. Yayin da rukunin D ya kunshi Morocco da Cote d'Ivoire da Afrika ta kudu da kuma Namibia.

Sai rukuni na E, inda Tunisia za ta kece raini da Eagles na Mali da Mauritania, wadanda suma suka shiga gasar a karon farko, sai kuma kasar Angola.

Kasar Kamaru kuma za ta kare kambunta ne da Black Stars ta Ghana da kasar Benin da kuma Guinea Bissau. (Fa'iza Mustapha)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China