in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
'Yan bindiga sun saci jami'an gwamnati a yankunan Kamaru masu fama da rikici
2019-03-04 11:08:19 cri

Wasu 'yan bindiga da ba a san ko su wane ne ba, sun saci wani babban jami'in gwamnati dake aiki a ofishin Gwamnan Buea, dake kudu maso yammacin kasar Kamaru, daya daga cikin yankunan kasar 2 dake da rinjayen masu amfani da Turanci, wanda kuma ke fama da rikici.

A cewar rundunar sojin kasar, 'yan bindigan sun saci Frankline Ngwa Che dake aiki a ofishin Gwamna dake kudu maso yammacin kasar ne da safiyar jiya Lahadi a gidansa.

Wata majiya daga rundunar da ta nemi a sakaya sunanta, ta ce mutanen da suka sace shi sun nemi a ba su miliyoyin kudin CFA a matsayin kudin fansa.

Har ila yau a jiyan, hukumomi a yankin arewa maso yammacin kasar, wanda shi ma ke fama da rikici, sun ce an saci shugaban ma'aikatar kare muhalli na kasar.

A cewar majiyar ta rundunar sojin, da alama yanzu masu satar mutanen jami'an gwamnati suke hari.

Sace-sacen mutane na kara kamari a yankunan 2 na arewa maso yamma da kudu maso yammacin Kamaru, inda 'yan aware masu dauke da makamai ke neman kafa sabuwar kasa da ake kira da "Ambazonia". (Fa'iza Mustapha)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China