in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Afrika na duba yuwuwar kara shigo da kayyaki kasar Sin ta hanyar bikin baje koli
2018-11-10 15:38:22 cri
Baje kolin kasa da kasa na kayayyakin da ake shigo da su kasar Sin wato CIIE da aka kammala a yau, ya ja hankalin 'yan kasuwa sama da 3,600 daga fadin duniya. Sama da 200 daga cikinsu sun fito ne daga kasashen Afrika sama da 40, inda suka baje kayayyakinsu daban daban, da suka hada da ganyen shayi da gahwa da barasa da Cocoa da abincin ruwa.

Babbar jami'ar zartaswar kamfanin Nyumbani Coffee, da ta halarci baje kolin, Fridah Mbaya, ta ce ta ji dadin zuwa Shanghai don halartar bikin CIIE, inda ta ce ya gabatar da kayayyakinta ga babbar kasuwa, musammam tsanakin al'ummar Sinawa.

Shi kuwa Koos Balaauw, daga kasar Namibia, ya CIIE a matsayin wanda ya samarwa 'yan kasuwa dandalin hadin gwiwa, don kamfanonin kasar Sin su zuba jari a kasashen Afrika, haka zalika su ma kamfanonin nahiyar, wanda ya ce na da nufin kara bunkasa kasashen ta hanyar kulla kawance don samun damar fitar da kayyaykinsu.

Cikin wani sakon email da ya aikewa kamfanin dillancin labarai na Xinhua, Keith Rock, draktan sashen yada labarai da hulda da jama'a na hukumar kula da cinikayya ta duniya WTO, ya ce bikin ya bayyana bukatar hadin gwiwa da kulla kawance a harkar cinikkayya tsakanin kasa da kasa, musammam kasar Sin da nahiyar Afrika. (Fa'iza Mustapha)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China