in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Al'ummar Afirka ta kudu sun bayyana ziyarar Xi a matsayin alaka mai karfi dake tsakanin kasashen biyu
2018-07-26 09:46:25 cri
Al'ummar kasar Afirka ta kudu sun bayyana cewa, ziyarar aikin da shugaban kasar Sin Xi Jinping ke yi a kasar wata alama ce dake nuna irin dangantakar diflomasiya da hadin gwiwa mai karfi dake tsakanin kasashen biyu.

A cewar mai magana da yawun shugaba Cyril Ramaphosa na Afirka ta kudu Khuselu Diko, kasashen biyu suna da tarihi na dadadden hadin gwiwa mai karfi bisa manyan tsare-tsare, inda ya ba da misali da alakar kasashen a bangaren kwamitin sulhun MDD da sauran harkokin da suka shafi tattalin arziki. Haka kuma kasashen sun daga matsayin alakarsu zuwa dangantakar manyan tsare-tsare, daya daga cikin alakar diflomasiya mafi girma.

Wani mai sharhi kan harkokin siyasar kasar Afirka ta kudu Somadoda Fikena na ganin cewa, ziyarar shugaba Xi a Afirka ta kudu za ta kara zurfafa alakar Sin da Afirka ta kudu, kasancewarsu mambobin BRICS baya ga alakar dake tsakaninsu a siyasance.

Ziyarar ta Xi dai wani bangaren ne na kara kyautata alakar siyasa da tattalin arziki , da jin dadin jama'a da ma hadin gwiwa a harkokin kasa da kasa tsakanin sassan biyu, kamar yadda fadar shugaban kasar Afirta ta kudun ta wallafa a shafinta na Twitter. (Ibrahim Yaya)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China