in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Shugaban kasar Sin ya karfafa al'ummar kasar gwiwar kokartawa
2018-03-20 19:24:06 cri
A yayin taron rufe taron farko na majalisar wakilan jama'ar kasar Sin karo na 13 da aka gudanar a yau Talata a nan birnin Beijing, shugaban kasar Sin Xi Jinping ya ce, al'ummar kasar Sin tun da da da can suka gane cewa, zaman alheri sai da kokartawa, kuma hikimarsu da kokarinsu ne suka kawo abubuwan da suke da su yanzu.

Ga kuma kalaman da shugaban taba ya yi wa al'ummar kasar daga sana'o'i daban daban.

'Yan jarida: Ku mai da al'umma a matsayin malamanku, ku sunkuyar da kai tare da yin natsuwa, ku sa ido a kan hakikanin halin da ake ciki, kuma ku fadi gaskiya, ku gabatar da labarai da ke da tunani da inganci, wadanda za su iya sosa ran al'umma.

Malamai:Ya kamata ku zama jagoran dalibai ta fannin gyara halinsu da samar musu ilmi da koya musu yadda za su yi kirkire-kirkire da kuma bauta wa kasarsu.

Ma'aikatar tsabta birane sun kasance masu gyaran fuskar biranen, wadanda suke gudanar da aiki mai tsarki da martaba. Ni ma mazauni birnin Beijing ne, don haka a madadin mazauna birnin, ina muku godiya.(Lubabatu)

 

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China