in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Libya: MDD ta bukaci kafa tsarin doka gabanin babban zabe
2018-02-09 09:56:06 cri
Mataimaki na musamman na babban magatakardar MDD a kasar Libiya Ghassan Salame, ya yi kira ga mahukuntan Libya da su kaddamar da tsarin kafuwar dokokin kasa, wadanda za su share fagen gudanar babban zaben kasar cikin nasara.

Mr. Ghassan Salame, ya yi wannan kira ne yayin wani taro da tawagar wakilan al'ummar Zawiyah, birni mai nisan kilomita 45 daga Tripoli fadar mulkin kasar ta Libya, taron da ya gudana a hedkwatar tawagar MDD mai aikin wanzar da zaman lafiya a kasar ko UNSMIL a takaice.

Jami'in ya ce ya kamata a gudanar da aikin rajistar masu kada kuri'a, da kuma kammala dokokin gudanar da kuri'un jin ra'ayin jama'a gabanin aiwatar da hakan.

A nasu bangaren, wakilai daga garin na Zawiyah sun gabatar da wasu batutuwa masu muhimmanci, wadanda za su taimaka wajen cimma daidaito, tare da kawo karshen rabuwar kai a fannin siyasar kasa. (Saminu)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China