in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Iraki ta sanar da 'yantar da dukkan wuraren dake karkashin mallakar IS
2017-12-10 13:43:49 cri
Jiya Asabar, rundunar sojan kasar Iraki ta sanar da cewa, sojojin gwamnati sun riga sun 'yantar da dukkan wuraren da suka taba zama karkashin ikon kungiyar IS, a halin yanzu kuma, yankin iyakar dake tsakanin kasar Iraki da kasar Syria baki daya yana karkashin ikon sojojin gwamnatin kasar.

A wannan rana kuma, babban kwamandan cibiyar bada jagoranci kan hadin gwiwar Iraki Abdul Amir Yarallah, ya fidda wata sanarwa inda ya bayyana cewa, a ranar 9 ga wata sojojin gwamnatin kasar da sojojin kungiyar mabiya Shi'a sun 'yantar da wani yankin dake tsakanin lardin Al-Anbar da lardin Ninewa, lamarin da ya nuna cewa, sun karbi ikon yankin iyakar dake tsakanin kasar Iraki da kasar Syria baki daya.

Mr. Yarallah ya kara da cewa, ya zuwa yanzu sojojin gwamnatin kasar Iraki sun 'yantar da dukkan wuraren da suka taba zama karkashin ikon kungiyar masu da'awar kafa daular musulunci ta IS. (Maryam)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China