in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Sin na duba na tsanaki game da rahoton kisan wasu 'yan kasar a Pakistan
2017-06-09 20:15:47 cri
Kakakin ma'aikatar harkokin wajen kasar Sin Hua Chunying, ta ce Sin na bin hanyoyi da suka dace, domin tantance sahihancin wasu rahotanni, wadanda ke cewa an hallaka wasu Sinawa biyu, bayan da aka yi garkuwa da su a watan da ya gabata a kasar Pakistan.

Hua Chunying ta ce tuni ofishin jakadancin kasar Sin dake Pakistan, ya fara gudanar da binciken gaggawa da hadin gwiwar mahukuntan kasar ta Pakistan, a wani mataki na tabbatar da kubutar da Sinawan da aka yi garkuwa da su.

Sai dai a hannu guda uwar gida Hua, ta ce bangaren Pakistan ya riga ya shaidawa Sin cewa, mai yiwuwa ne masu garkuwa da mutanen sun riga sun hallaka su.

Ta ce kasar Sin na matukar adawa da duk wani nau'in aiki na ta'addanci, za kuma ta ci gaba da hada kai da Pakistan, a duk wani mataki na yaki da ayyukan 'yan ta'adda da kuma tabbatar da tsaro da daidaito a kasar.

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China