A Larabar nan ne kakakin ma'aikatar harkokin wajen kasar Sin Geng Shuang, ya bayyana cewa Sin ta riga ta tuntubi kasar Indiya a hukumance, dangane da batun yankin Taiwan.
Geng Shuang ya fadi haka ne a yayin taron manema labaru da aka saba shiryawa a nan Beijing, inda ya ce kasar Sin na fatan Indiya za ta bi manufar "kasar Sin daya tak a duniya", za kuma ta yi taka tsan-tsan yayin da take daidaita batun Taiwan.
An labarta cewa, yanzu haka 'yan majalisar kafa dokokin yankin Taiwan 3 na ziyara a kasar Indiya, inda kuma suka gabatar da shawarar "daga matsayin hukumar Taiwan da ke Indiya". (Tasallah Yuan)