Sahin ya ce wani dan bindiga ne ya kaddamar da harin shi kadai.
Wani mai sharhi kan al'amurran tsaro wanda ya nemi a sakaye sunansa, ya shedawa kamfanin dillancin labarai na Xinhua cewa, maharin ya harbe mai gadin gidan rawar, daga nan kuma ya kutsa kai gidan rawar inda ya bude wuta, wajen na cike makil da jama'a sama da mutane 400 wadanda ke gudanar da bikin murnar zuwan sabuwar shekara. (Ahmad Fagam)