in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Kungiyar wasan kwallon kafan mata ta Nijeriya ta zama zakara a gasar cin kofin Afirka mata ta 2016
2016-12-04 13:43:32 cri

An kammala gasar cin kofin Afirka mata ta shekarar 2016 a birnin Yaounde na kasar Kamaru a jiya ranar 3 ga wata a filin wasa na Ahmadou Ahidjo, a karshe dai kungiyar wasan kwallon kafa mata ta kasar Nijeriya ta doke kungiyar kasar Kamaru da ci daya mai ban haushi, tare da zama zakara a wannan karo. Kamaru ta zama na biyu kuma Ghana ta zama na uku.

Shugaban kasar Kamaru Paul Biya ya halarci bikin rufe gasar kallon da aka kawo karshenta.

Kungiyoyi 8 sun halarci gasar a wannan karo, wadanda suka raba a cikin rukunoni biyu. A rukunin A, ya kunshi Kamaru, Masar, Zimbabwe, Afirka ta Kudu. Kana rukunin B, ya hada Nijeriya, Mali, Kenya da Ghana. Kamaru da Nijeriya sun zama matsayin farko a rukuninsu da shiga wasan dake kusa da na karshe, kuma sun cimma nasarar wasan tare da kuma fafatawa a wasan karshe.

Hukumar wasan kwallon kafa ta Afirka na shirya gasar cin kofin Afirka mata a shekaru biyu biyu tun daga shekarar 1998. (Zainab)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China