Kwallon da Moses din ya ciwa Chelsea a wannan wasa ita ce ta biyu, da ya zura a raga a gasar Firimiya ta bana, sai dai duk da hakan Obi na ganin nan gaba kadan, dan wasan zai samu cikakken gurbi a kungiyar, bayan da a baya ya bugawa kulaflikan Liverpool, da Stoke City wasa a matsayin dan wasan aro.(Saminu Alhassan)