in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
An kammala taron G20 a birnin Hangzhou na kasar Sin
2016-09-26 07:20:48 cri

A kwanakin baya ne aka rufe taron koli na G20 a birnin Hangzhou na kasar Sin. An dai cimma muhimman sakamako masu yawa da kuma matsaya daya a tsakanin kasashe daban daban a fannoni da dama a yayin taron, batutuwan da suka samu jinjina da amincewa sosai daga kasashen duniya. Shugaban kasar Sin Xi Jinping ya bayyana a cikin jawabinsa a gun bikin rufe taron kolin na G20 cewa, shugabanni da manyan jami'an kasashe membobin kungiyar G20, da kungiyoyin kasa da kasa, sun yi musayar ra'ayi sosai kan ayyukan kirkiro sabbin fasahohi, da gudanar da hadin gwiwa a fannin tattalin arziki a cikin kwanaki biyu da aka shafe ana taron, domin tattaunawa kan shirin raya tattalin arzikin duniya.

Masana na nuna cewa, an gudanar da taron kolin G20 na birnin Hangzhou ne a yayin da tattalin arzikin duniya ke kara fuskantar sauye-sauye, da kuma kokarin ganin an aiwatar da gyare-gyare kan kungiyar G20.

Mahalarta taron kolin G20 sun tsara shirin bunkasuwar cinikayya a duniya, da kuma takardar ka'idojin zuba jari ta G20, wanda ya zama tsarin zuba jari na farko na duniya, kana za a ci gaba da goyon bayan tsarin cinikayya a tsakanin kasashe daban daban, da kuma nanata alkawarin nuna adawa da ba da kariya ga tattalin arziki. Ana sa ran tattalin arzikin duniya zai samu farfadowa ta hanyar inganta cinikayya da zuba jari a duniya.

Masu fashin baki na cewa, bisa kokarin da bangarori daban daban suka yi, an cimma nasarar wannan taron da ya kasance mafi kayatarwa a tarihin kungiyar, kuma za a ci gaba da aiwatar da sakamakon da aka samu a gun taron, domin tabbatar da neman samun bunkasuwar tattalin arzikin duniya mai dorewa. (Ada, Saminu, Ibrahim/Sanisu Chen)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China