in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Kasar Sin na taka muhimmiyar rawa ga aikin raya muhimman ababen more rayuwa na Afirka, in ji wani jami'in Afirka
2016-07-16 17:48:42 cri

Wata babbar jami'ar kwamitin kula da harkokin kungiyar AU ta bayyana jiya Jumma'a, cewa kasar Sin na taka muhimmiyar rawa ga aikin raya muhimman ababen more rayuwar kasashen Afirka.

Elham Mohmood Ibrahim, wata jami'a mai kula da muhimman ababen more rayuwa da makamashi a kwamitin kula da harkokin kungiyar AU ta bayyana a yayin taron manema labarai da aka kira kafin kaddamar da taron koli na 27 na AU, cewar kasashen Afirka na son yin hadin gwiwa tare da dukkan abokansu wajen raya muhimman ababen more rayuwa. A ganinta, hadin kan Sin da Afirka ya dace da manufar samun nasara tare.

Ta kuma kara da cewa, a 'yan shekarun nan, kasar Sin ta sa hannu cikin ayyukan raya muhimman ababen more rayuwa na kasashen Afirka da yawa, kungiyar AU na maraba da irin hadin gwiwar Sin da Afirka a wannan fanni, kuma tana sa ran ganin gudanar da irin wadannan ayyuka nan gaba. (Kande Gao)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China