in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
AU tana shirin kaddamar da hukumar kula da harkokin magunguna ta Afirka
2016-06-09 12:50:23 cri
A jiya ne wata tawagar kwararru ta kammala ganawa ta kwanaki 2 da nufin kaddamar da hukumar kula da magunguna ta Afirka.(AMA)

A yayin ganawar wadda ta gudana a hedkwatar kungiyar AU da ke birnin Addis Ababa na kasar Habasha daga ranar 7 zuwa 8 ga wata, tawagar ta tattauna batutuwan da suka shafi shata taswirar da za ta kai ga kaddamar da wannan hukuma.

A cikin watan Afrilun shekarar 2014 ne ministocin kiwon lafiya na kasashen Afirka suka amince a kafa hukumar kula da magunguna ta Afirka,wadda za a dora mata alhakin sanya ido kan irin kayayyakin kiwon lafiya da suke wadari a kasuwannin Afirka.

Bugu da kari, ana sa ran hukumar ta kasance babbar mai sanya ido wajen magance kayayyakin lafiya na jabu, baiwa magungunan da ake sarrafa a cikin gida damar yin takara, musamman magungunan cututtukan da ke damun kasashen Afirka.(Ibrahim)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China