in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Shugaban Saliyo ya karrama takwaransa na Sin da babbar lambar yabo ta kasar
2016-05-16 10:33:02 cri

Kwanan baya ne, shugaban kasar Saliyo Ernest Bai Koroma ya shirya biki a fadarsa don karrama takwaransa na kasar Sin Xi Jinping da lambar yabo ta koli ta kasar wato GCOR, a madadin gwamnatin Saliyo da jama'arta.

Jakadan Sin a kasar Zhao Yanbo ya karbi lambar yabon a madadin shugaba Xi na kasar Sin. Mataimakin shugaban kasar da raguwar majalisar ministocin kasar da sauran jami'an diplomasiyya na kasashen waje da ke kasar sama da 100 sun halarci wannan biki.

A lokacin da ya ke mika lambar yabon, shugaban Koroma ya bayyana cewa, gwamnatin Sin karkashin shugabancin Xi Jinping, ta ba da gudummawa da agajin jin kai ga kasar Saliyo, lamarin da ya ingiza bunkasuwar kasar, musamman ma aniyar shugaban Xi ta ba da agaji da fasahohi cikin lokaci ga kasar Saliyo wajen tinkarar cutar Ebola, abun da ya nuna hadin gwiwar kasashen biyu.

Shugaban Koroma ya tsaida kudurin karrama shugaba Xi Jinping da babbar lambar yabon ne domin nuna godiya ga kasar Sin. A madadin shugaba Xi, jakadan Zhao ya karbi lambar yabon da takardar shaida, daga bisani ya mika godiyar shugaba Xi ga shugaba Koroma.(Bako)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China