in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Kungiyar IGAD na goyon bayan matakan yaki da tsattsauran ra'ayi na MDD
2016-01-21 10:47:14 cri
Kungiyar shuwagabannin yankin gabashin Afirka ta IGAD, ta jinjinawa kokarin da MDD ke yi game da yaki da ayyukan tsattsauran ra'ayi, domin cimma nasarar wanzar da tsaro da zaman lafiya a duniya.

Wata sanarwar da babban sakataren kungiyar ta IGAD Mahboub Maalim ya fitar a birnin Nairobin kasar Kenya, ta bayyana amincewarsa da manufofin yaki da tsattsauran ra'ayi, wadanda babban magatakardar MDD ya gabatar a kwanakin baya, matakin da ke da nufin kandagarki, tare da fuskantar kalubalen da 'yan ta'adda ke haifarwa ga rayuwar bil'Adama.

Sanarwar ta kuma bayyana bukatar dake akwai, ta hada karfi da karfe da daukacin kasashen duniya, wajen dakile dalilan da ke haifar da yaduwar tsattsauran ra'ayi, kamar yadda hakan ke kunshe cikin tsarin zartaswa na MDD.

Maalim ya jaddada cewa, zartas da manufofin dake kunshe cikin tsarin na MDD, na bukatar hadin kai daga sassan masu ruwa da tsaki a mataki na shiyya-shiyya da kuma na kasa da kasa.

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China