in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Allassane Ouattara ya sake lashen zaben shugaban kasar Cote d'Ivoire
2015-10-28 15:58:18 cri
Sakamakon babban zabe na zagaye na farko da hukumar zabe mai zaman kanta ta Cote d'Ivoire ta bayar a safiyar yau, ya nuna cewa shugaba mai ci yanzu Alassane Ouattara ya sake lashe zaben shugaban kasar da kashi 80 cikin 100 bisa yawan kuri'un da ya samu.

Bisa sakamakon wucin gadi da aka bayar, an ce, dan jam'iyyar kawacen hadin kan 'yan kasa ta Républican, kana shugaba mai ci na yanzu Alassane Ouattara ya samu kuri'un da yawansu ya kai miliyan 3.1, wadanda suka tashi zuwa kashi 83.66 cikin 100, wanda ya ba shi galaba kan abokin hamayyarsa Pascal Affi N'Guessan dan jam'iyyar adawa ta FPI.

An gudanar da zaben shugaban kasar a ranar 25 ga wata, kuma yawan masu kada kuri'u da suka yi rajista ya kai sama da miliyan 6.3, kuma yawan kuri'un da aka samu ya kai kashi 54.63 cikin 100.

Kwamintin tsarin mulki na Kwadivoire zai bayar da sakamakon zabe a gaban bainar jama'a har na tsawon kwanaki 8, idan babu rarrabuwar kawuna, kwamitin zai sanar da cewa, Ouattara ya sake cin zabe a hukunce.(Bako)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China