in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
WFP da ma'aikatar harkokin noma ta Sin sun fara horas da dabarun noma da adana amfanin gona
2015-10-13 20:19:06 cri
A yau ne a nan birnin Beijing na kasar Sin shirin samar da abinci na duniya WFP da ma'aikatar harkokin noma ta kasar Sin tare da hadin gwiwar kasashe masu tasowa suka fara wani shirin horas da fasahohin noma da kuma dabarun adana amfanin gona,

Shirin na sa ran horas da jami'ai daga kasashen Uganda, Tanzania, Zambia da wasu kasashen Afirka, ta yadda za a kyautata fasahohinsu na aikin gona da kuma yadda za su inganta dabarun adana amfanin gona da yin rigakafin hadarin da abin ya shafa.

Haka kuma, shirin na WFP zai zurfafa hadin gwiwar dake tsakaninsa da kasar Sin, domin gabatar da fasahohin kasar Sin a fannin aikin gona cikin kasashen duniya, ta yadda za a taimaka wajen kawar da matsalar karancin abinci a duniya da kuma ciyar da hadin gwiwar kasashe masu tasowa gaba. Haka kuma, ana sa ran gabatar da irin fasahohin da kasashen duniya suka samu a lokacin wannan horo ga yankunan kasar Sin dake fama da karancin abinci a halin yanzu. (Maryam)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China