in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Xi Jinping ya bukaci a dukufa wajen ba da jinya ga wadanda fashewar wasu abubuwa a birnin Tianjin ta shafa
2015-08-13 14:23:44 cri
A jiya da dare ne wasu abubuwa da ake zato sinadarai makare a cikin wata kwantena suka yi bindiga a tashar jiragen ruwa da ke birnin Tianjin da ke bakin teku.

Ya zuwa karfe 12 na ranar yau, fashewar ta haddasa rasuwar mutane guda 44, ciki hada da 'yan aikin kwana-kwana guda 12, kana wasu mutane 520 suna karbar jinya a asibiti, 66 daga cikinsu suna ji rauni mai tsanani.

Fashewar ta auku ne a wani dakin da ake ajiye sinadarai masu matukar hadari, kuma rahotanni sun nuna cewa, gine-gine, wuraren ajiye motoci da wasu wuraren da ke kusa da wurin fashewa sun kama da wuta sakamakon fashewar.

Har zuwa yau da safe ana iya ganin wuta na ci yayin da hayaki ya turnuke wurin, yayin da a wasu lokutan gilasai ke fadowa daga sama , haka kuma, fashewar ta lalata kamfanoni guda shida dake kusa da wurin. Ana kuma kiyasin cewa,kashi daya bisa shida na motoci dubu shida da ake wani wurin ajiye motoci sun kone. (Maryam)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China