in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Yawan mutanen da suka kamu da cutar Ebola a yammacin Afrika ya kai fiye da dubu 20
2014-12-30 15:09:33 cri

Bisa kididdigar da hukumar kiwon lafiya ta duniya WHO ta bayar a ran 29 ga wata, an nuna cewa, ya zuwa ran 27 ga wata yawan mutanen da suka kamu da cutar Ebola a kasashen uku na yammacin Afrika wato Saliyo, Laberiya, Guinea ya kai 20081, daga cikinsu mutane 7842 sun mutu.

A halin yanzu, kasar Saliyo ta zarce Laberiya da yawan mutanen da suka kamu da cutar Ebola, wadanda yawansu ya kai 9409, daga cikinsu 2732 sun mutu. A dalilin haka ne ma, kasar ta Saliyo ta soke duk wasu bukukuwan bikin Kirismas da na shiga sabuwar shekara domin hana yaduwar wannan cuta. (Amina)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China