in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Mutane 68 sun rasu sanadiyyar fashewa a wata masana'antar dake birnin Kunshan na Sin
2014-08-02 20:44:27 cri
Bisa labarin da aka samu a yau Asabar 2 ga wata, an ce, wani abu ya fashe a masana'antar karafa ta Zhongrong dake birnin Kunshan na kasar Sin tare da haddasa mutuwar mutane guda 68, yayin da sama da187 suka jikkata, kuma an riga an kai 137 daga cikin wadanda suka jikkata zuwa biranen Suzhou, Shanghai, Nantong da dai sauran wurare domin ba su jinya.

Kuma bisa labarin da ma'aikatar kiyaye zaman lafiyar jama'a ta kasar Sin ta fitar, an ce, haduwar kurar karafa da wuta ce ta haddasa fashewar a masana'antar.

Kaza lika, a yau Asabar 2 ga wata, bisa umurnin shugaban kasa Xi Jinping da firaminista Li Keqiang, wakilin majalisar gudanarwar kasar Sin Wang Yong da wasu jami'an hukumomin gwamnati da abin ya shafa sun isa wurin da wannan hadari ya faru cikin gaggawa domin jagorantar ayyukan ba da agaji da wasu ayyukan makamantan haka na gaggawa. (Maryam)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China