in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Karin shugabannin kasashen duniya na taya Xi murnar zabensa a matsayin babban sakataren JKS
2012-11-18 16:58:51 cri
Xi Jinping na ci gaba da samun sakonnin taya murna daga sassa daban daban na duniya sakamakon zabarsa da aka yi a matsayin babban sakataren kwamitin tsakiya na JKS.

A cikin sakonsa na taya murna ga Mr. Xi, shugaban Najeriya Goodluck Jonathan, ya lashi takwabin yin aiki kafada da kafada da sabon shugaban na kasar Sin, ta yadda za a bunkasa harkokin cinikayya da tattalin arziki tsakanin kasashen biyu.

Shugaban na Najeriya ya ce, gwamnatinsa za ta ci gaba da nuna kulawa da irin taimakon da gwamnatin Sin ke baiwa Najeriya kamar a sassan da suka shafi kayayyakin more rayuwa, makamashi, sufuri da kuma sadarwa.

Shi ma a sakonsa na taya murna, shugaba Mahamadou Issoufou na jamhuriyar Niger, ya ce manufofin JKS, da suka shafi bude kofa ga kasashen waje, sun taka muhimmiyar rawa ga irin nasarorin da kasar Sin ta samu a fannoni daban-daban tare da zama daya daga cikin kasashe masu karfin tattalin arziki a duniya.

Shugaba Issoufou ya bayyana kudurinsa na kara kokarin hada kai da Xi don kara karfafa dankon zumunci da hadin kai tsakanin kasashen biyu da kuma al'ummominsu.

A sakonsa na murna ga Xi Jinping shugaba Bai Koroma na Saliyo kana shugaban jam'iyyar APC, ya ce, "a madadin ni kaina, gwamnati da al'ummar jamhuriyar Saliyo, ina taya ka farin ciki tare da kasancewa cikin koshin lafiya, kuma ina fatan cewa, dankon zumuncin da ke tsakanin kasashen biyu zai ci gaba". (Ibrahim)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China