An yi kira ga shugabannin Afirka da sauran shugabannin kasashe, da su yi koyi da fasahohin da kasar Sin ta amfani da su wajen inganta rayuwar al'ummomin kasashensu.
Dr. Otaki Osana Alanana, malami a jami'ar Abuja da ke tarayyar Najeriya ne ya bayyana hakan yayin wata zantawa da wakilin sashen hausa na CRI da ke Abuja, wato Danladi.
Dr. Otaki Osana Alanana ya kuma bayyana irin matakai da kwarewar da kasar Sin ta yi amfani da su wajen tinkarar duk wasu kalubale da suka kunno kai a kasar.
Ga yadda hirar tasu ta kasance…..