in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Wasu shugabanni, jam'iyyu da kungiyoyi na kasashen Afirka sun taya JKS murnar bude babban taron wakilai karo na 18
2012-11-09 20:30:55 cri
A yayin da ake gudanar da babban taron wakilan jam'iyyar Kwaminis ta kasar Sin karo na 18 a nan birnin Beijing, kwanan baya wasu shugabanni, jam'iyyu da kungiyoyi na kasashen Afirka sun aiko da wasikun fatan alheri ko kuma sakwannin tangarahu domin taya jam'iyyar murnar bude babban taron wakilanta.

Johnson Aseidu Nketia, babban darektan jam'iyyar NDC ta kasar Ghana ya bayyana cikin wasikarsa ta fatan alheri cewa, JKS ta dace da yanayin da ake ciki ta fuskar siyasa, tattalin arziki, al'adu da dai sauransu. Jam'iyyarsa na son ci gaba da raya huldar kud-da-kud da JKS, tare da inganta zumunci da hadin gwiwa a tsakanin kasashen 2 da jama'arsu duka.

Ban da wannan kuma, a cikin wasikarsa ta fatan alheri, Omer Hassan Ahmed El Bashir, shugaban jam'iyyar babban taron kasar Sudan kuma shugaban kasar ya ce, babban taron wakilan JKS karo na 18 na da matukar muhimmanci, wanda zai himmantu wajen tabbatar da ganin jama'ar Sin sun ji dadin zaman rayuwarsu, ana raya kasa ta hanyar kimiyya, al'ummomin kabilu daban daban na kasar sun hada kansu domin aiwatar da fasahohin raya kasa, har wa yau kuma, a yayin da ake gudanar da taron, ana samun muhimman sauye-sauye a kasa da kasa, inda kasar Sin da ma jam'iyyar Kwaminis ta kasar Sin suke taka muhimmiyar rawa mai yakini. (Tasallah)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China